Connect with us

Ƙetare

AU ta dakatar da ƙasar Madagascar daga ƙungiyar

Published

on

Tarayyar Afirka AU, ta dakatar da ƙasar Madagascar daga ƙungiyar bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a ranar Talata.

Hakan na zuwa ne bayan majalisar dokokin ƙasar ta tsige shugaba Andry Rajoelina bayan ya tsere daga ƙasar sanadiyyar ƙazancewar zanga-zanga.

Ba da daɗewa ba ne wata tawagar sojoji ta karɓe iko da ƙasar, inda ta yi alƙawarin gudanar da zaɓe cikin shekaru biyu.

Rahotonni sun bayyana cewa, zanga-zangar rikicin siyasa mafi muni da ta dabaibaye ƙasar cikin shekarun baya-bayan nan, bayan kwashe makonni ana zanga-zanga kan matsanancin ƙarancin lantarki da ruwa, inda masu zanga-zangar suka buƙaci shugaba Rajoelina ya sauka daga mulki.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!