Connect with us

Labarai

Ayyana  ƴan takara da jam’iyyu ke yi a tsakiyar mulki ya saɓa dokokin zaɓe-INEC

Published

on

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Najeriya INEC,  ta ce ayyana  ƴan takara da jam’iyyu ke yi tun a tsakiyar wa’adin mulki ya saɓa da dokokin zaɓe.

A cewar hukumar,  kamata ya yi a bari masu mulki su sauke nauyin alƙawurran da suka ɗauka a lokacin yaƙin neman zaɓensu na baya, maimakon fara gangamin zabe na 2027 tun kafin lokaci yayi.

INEC, ta yi wannan jan hankalin ne bayan yawaitar al’amuran masu kama da yaƙin neman zaɓe a tsakanin jam’iyyu da kuma ƴan siyasar ƙasar, dake  ciigba da wakana a fadin kasar.

Sanarwar ta INEC, wadda ta fitar a baya-bayan na zuwa ne biyo bayan yadda aka ga gwamnoni da ‘ƴan majalisa da wasu jiga-jigan jam’iyyar APC mai mulki a kasar  suka sanar da cikakken goyon bayan su ga sake tsayawar shugaba Tinubu takara a zaɓe mai zuwa,  da suka jaddada cewa babu wanda zai fito domin karawa da shi wajen neman kujerar a cikin jam’iyyar su.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!