Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

INEC:baza mu daga zabe don canza ‘yan takara ba

Published

on

Hukumar zabe mai zaman kanta ta Najeriya INEC ta ce ba za ta daga lokutan zabe ba biyo bayan umarnin da kotunan kasar nan suka bayar na maye guraban wasu yan takarar da wasu.

Shugaban hukumar Farfesa Mahmud Yakube ne ya sanar da hakan ya yin zauren masu ruwa da tsaki kan shirin gudanar da zabe na bana da hukumar ta shirya aka gudanar a birnin tarayya Abuja.

Ya cu hukumar ta na ta karbar umarni da ga kotuna daban-daban na musanya wasu yan takarar da wasu, yayinda wasu umarnin ma ke cin karo da juna.

Ya kuma ce humar ta INEC tana aiki ne da abin da ya zo mata na karshe don haka bata bukatar wani al’amari da zai dauki lokaci.

Farfesa Yakubu ya kuma ce zaben fidda gwani da jam’iyyun suka gudanar a wannan karon shi ne mafi rudani da aka taba samu a Najeriya tun bayan dawowar mulkin dimukuradiyya Najeriya a shekarar 1999 inda hukumar ta INEC ta karbi hukuncin kotu har 640.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!