Connect with us

Labarai

Ba ma bukatar rancen kudi na TISSF- ASUU

Published

on

Ƙungiyar Malaman jami’o’i ta Najeriya ASUU, ta bayyana ƙin amincewarta da sabon shirin da Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar na bayar da lamunin kuɗi ga ma’aikatan jami’o’i, na Tertiary Institutions Staff Support Fund TISSF.

Shugaban ƙungiyar, Farfesa Christopher Piwuna, ya bayyana cewa membobin ASUU ba sa buƙatar wannan bashi, illa dai a inganta albashi da yanayin aiki. 

ASUU ta yi gargadi cewa tsarin aron zai ƙara matsaloli ga malamai, musamman ganin yadda ake riga da cire kuɗaɗen fansho, lafiya da kuma na ƙungiyoyi daga albashin su. Ƙungiyar ta ce wannan zai iya lalata harkokin haɗin gwiwar ƙungiyoyi  da malamai ke dogaro da su.

Kungiyar ta kuma sanar da shirinta na gudanar da zanga-zangar gargadi a jami’o’i a mako mai zuwa, tare da jan kunne cewa idan gwamnati ba ta ɗauki matakin da ya dace ba a taron da aka shirya yi a ranar 28 ga Agusta, 2025, to za a iya shiga sabon yajin aiki.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!