Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Ba mu da shirin tafiya yajin aiki – IPMAN

Published

on

Kungiyar dillalan man fetur ta kasa, IPMAN, shiyyar jihar Kano, ta ce bata da shirin tafiya yajin aiki saboda karin kudin man fetur da gwamnatin tarayya ta yi cikin makon jiya.

Shugaban kungiyar, shiyyar Kano, Alhaji Bashir Dan-Malam ne ya bayyana haka a ranar Litinin, jim kadan bayan kammala shirin ‘Barka da Hantsi na nan tashar Freedom Rediyo da ya maida hankali kan karin farashin man fetur zuwa Naira 145 kowace lita daya.

Alhaji Bashir Dan-Malam ya ce karin kudin man fetur din da gwamnati tayi ba zai rasa nasaba da yadda aka samu karin yawan man a kasuwar duniya ba.

Labarai masu alaka:

Al’umma su kwantar da hankulan su-IPMAN

Gwamnatin tarayya ta kafa kwamiti nazarin matsalar karancin man fetur

Shugaban IPMAN ya kara da cewa duk lokacin da aka samu man gwamnati na kara firiashin don radin kanta, a don haka ya yi kira ga abokan huldarsu da su fahimci cewa karin ba daga wajensu yake ba.

Dan-Malam ya yi fatan karin da aka yi na kwanan nan ba zai jawo wata matsala ba a bangaren gudanar da al’amuran yau da kullum na jama’a ba.

 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!