Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ba wani alƙawari tsakanina da Atiku – Shekarau

Published

on

Tsohon Gwamnan Kano Malam Ibrahim Shekarau ya yi watsi da raɗi-raɗin cewa ɗan takarar Shugaban ƙasa a PDP Alhaji Atiku Abubakar ya bashi miliyoyin kuɗaɗe.

Shekarau ya bayyana hakan ne a zantawarsa da manema labarai a ranar Lahadi.

Ya ce, ana ta ƙarairayi, wasu su ce Atiku ya bashi kuɗi, wasu kuma sun ce an siya masa gida Abuja.

Malam Shekarau ya ce, duk waɗanda ke faɗar hakan basu san shi ba, ko kuma sun zalunce shi.

Ya ce, lokacin da yana Principal su suke yin bajet, abin da yake iya yi a lokacin yanzu Kwamishina baya yi.

Tsawon wancan lokaci har na zo nayi gwamna na gama ban taɓa haɗa baki da wani ɗan Kwangila ba, kan ya kawo mu kuɗi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!