Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Da dumi-dumi: Shekarau ya fice daga NNPP zuwa PDP

Published

on

Sanatan Kano ta tsakiya Malam Ibrahim Shekarau ya fice daga jam’iyyar NNPP zuwa Jam’iyyar PDP.

Malam Shekarau wanda  tsohon gwamnan ne ya bayyana ficewar ta sa, yayin wani taro na musamman da ya gudanar a gidan sa dake mundubawa yau Litini.

Tuni dai Malam Ibrahim Shekarau din ya samu tarba daga dan takarar shugabancin kasar nan a jam’iyyar ta PDP Alhaji Atiku Abubakar wanda ya zo Kano domin karbarsa.

Da yake yi masa maraba a jam’iyyar, Atiku Abubakar ya ce, shigowar yan siyasa irin su Shekarau a jam’iyya babbarb nasara ce da kuma ci gaban jam’iyyar.

Idan za a iya tunawa dai Malam Ibrahim Shekarau bai dade da yiwa jam’iyyar NNPP mubaya’a ba, sai kuma ya sake sauya sheka zuwa PDP sakamakon abin ya kira rashin adalci a jam’iyyar NNPP.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!