Connect with us

Labarai

Ba za mu amsa gayyatar majalisa ba- Gwamnonin Zamfara da Benue

Published

on

Gwamnan jihar  Zamfara Dauda Lawan Dare da takwaransa na  Benue  Hyacinth Alia, sun ce ba za su amsa gayyatar da Kwamitin karɓar ƙorafe-ƙorafe na Majalisar Wakilai ya yi musu ba,  sakamakon shakku kan halaccin gayyatar.

A baya dai Majalisar ta  gayyaci gwamnonin da majalisun dokokin jihohin su ne domin su bayyana a gaban kwamitin bisa zargin saba kundin tsarin mulki da gazawa wajen gudanar da mulki, da kuma fama da matsalar tsaro da rikici tsakanin wasu ‘yan majalisar dokokin jihohin.

Gayyatar na kunshe ne a wata sanarwa da shugaban kwamitin yada labarai da korafe-korafe na majalisar wakilan, Chooks Oko, ya fitar ranar Juma’ar da ta gabata.

Haka kuma gayyatar ta bukaci sanin ko suna da ja kan kudurin majalisar wakilan na karbe ikon gudanar da ayyukan majalisun jihohin biyu, kamar yadda sanarwar ta ce sashe na 11, (4) cikin Baka na kundin tsarin mulkin kasar  na 1999 ya bayar da dama.

Sai dai, a jihar Benue, akwai takaddamar dakatar da wasu ‘yan majalisar jihar 13, wadanda ba sa jituwa da gwamnan jihar, yayinda a  jihar Zamfara  aka samu majalisa biyu, inda wasu ‘yanmajalisa tara suke ikirarin damar ci gaba da aikinsu duk da cewa an dakatar da su.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!