Connect with us

Labarai

Ba za mu biya ma’aikata albashin Afrilu ta banki ba- Gwamnatin Kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta ce, ba za ta biya ma’aikatanta albashin watan nan da muke ciki na Afrilu ta hanyar banki ba, maimakon haka za a biya su ne kai tsaye ta hanyar tantance su a hukumomin da su ke aiki.

Sakataren gwammatin Kano Alhaji Umar Faruk Ibrahim, ne ya bayyana hakan lokacin da ya ke jawabi ga manema labarai dangane da gano ma’aikatan kananan hukumomi sama da dari biyu da suka bar aiki wasun su suka rasu amma ana ci gaba da biyan albashi a asusun su.

Alhaji Umar Faruk Ibrahim ya ce, gwamnati za ta gayyaci ma’aikatan da aka gano suna karbar albashi sau biyu a ma’aikatar da suke aiki don yin bayani.

Haka kuma Sakataren gwamnatin ya ce, gwamnati za ta magance yadda ake bai wa ma’aikata bashin kaya sakamakon gano yadda ake cutar da su a fannin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!