Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ba zan sake tsayawa takara a 2023 ba – Gwamna Masari

Published

on

Gwamnan Katsina Aminu Bello Masari ya yi watsi da raɗe -raɗin da ake yi cewa zai ƙara tsayawa takarar neman wani muƙamin siyasa a kakar zaben 2023.

Gwamnan ya bayyana hakan yayin zantawarsa da manema labarai.

Masari ya ce, matuƙar ya kammala wa’adin sa na biyu ba zai sake tsayawa takarar neman kujerar siyasa ba, sai dai zai goyi bayan matasa masu tasowa da su tashi tsaye don neman muƙaman siyasa da shugabancin jama’a.

“Ba zan yi takarar kowane muƙami ba a cikin jam’iyya ko a gwamnati, na kasance shugaban majalisar dokoki ta ƙasa don haka bana sake sha’awar komawa cikin ta” in ji Masari.

“A cikin jam’iyyar APC ma ni ne mataimakin shugaban jam’iyyar na ƙasa shiyyar Arewa don haka wane matsayi zan ƙara nema a jam’iyyar?” A cewar Masari.

Gwamnan Katsinan ya ce, lokaci ya yi da za a ƙyale matasa masu tasowa su taka ta su rawar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!