Labarai
Babban hafsan sojan Najeriya ya shawaraci mutane su laƙanci dabarun kare kai

Babban hafsan hafsoshin Kasar nan, Janar Christopher Gwabin Musa, ya shawaraci ƴan Najeriya da su laƙanci dabarun kare kai daga haɗurra a matsayin mataki na ko-ta-kwana.
Janar Christopher Gwabin Musa ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa da kafar talabijin ta Channels a jiya Alhamis.
Matsalar tsaro na addabar yankuna da dama na Najeriya, inda masu ɗauke da makamai ke kashe mutane tare da tarwatsa su daga muhallansu.
Duk da cewa hukumomi na cewa suna bakin ƙoƙarinsu, amma lamarin na ci gaba da laƙume ɗaruruwan rayuka a yankunan da ake fama da irin waɗannan tashin-tashina, kamar arewa maso yamma da arewa maso gabas da kuma arewa ta tsakiyar.
Ko a ranar Litinin da ta gabata, wasu mahara sun kashe masu ibada aƙalla 28 a wani masallaci da ke karamar hukumar Malumfashi da ke jihar Katsina, arewa maso yammacin ƙasar.
Haka nan a watan da ya gabata masu garkuwa da mutane sun yi wa mutum 38 yankan rago cikin waɗanda suke garkuwa da su a jihar Zamfara mai maƙwaftaka.
You must be logged in to post a comment Login