Labarai
Babban Hafsan Tsaro ya tura Runduna ta musamman zuwa Kwara da Neja

Babban Hafsan Tsaron kasar nan , Janar Olufemi Oluyede, ya ce za a tura rundunar sojoji ta musamman zuwa Jihar Kwara da wasu sassan Jihar Neja domin magance Kalubalen tsaro.
Shugaban ya bayyana hakan ne yayin gabatar da bitar kasafin kuɗin 2025 da kuma ƙudirin kasafin 2026 a gaban Kwamitin Tsaro na Majalisar Wakilai.
Janar Oluyede ya ce sojoji sun samu nasarori wajen yaƙar ‘yan ta’adda da masu garkuwa da mutane, sai dai domin ɗorewar zaman lafiya dole ne a ƙara ƙarfafa rundunar ‘yansanda da Hukumar tsaro ta NSCDC domin su riƙe yankunan da aka ƙwato.
Ya kuma ce an riga an tura runduna ta musamman zuwa jihohin Benuwe da Filato, sannan za a ƙaddamar da wata sabuwar rundunar haɗin gwiwa mai suna Operation Savannah Shield domin aiki a Kwara da wasu sassan jihar Neja.
Babban hafsan ya ƙara da cewa sojoji na fuskantar ƙarancin ma’aikata, don haka akwai buƙatar ƙarin haɗin kai da isasshen tallafi domin inganta tsaro a faɗin ƙasar.
You must be logged in to post a comment Login