Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Babban Jojin Najeriya ya sha alwashin yaki da cin hanci da rashawa

Published

on

Babban Jojin Najeriya Tanko Muhammad ya lashi takobin yaki da duk wani nau’i na cin hanci da rashawa da ke cikin hukumar shari’ar kasar nan.

Tanko Muhammad ya shaida hakan ne lokacin da yake zantawa da manema labarai na fadar shugaban kasa jim kadan bayan da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya rantsar da shi jiya a Abuja.

Ya kuma bayyana hukumar shari’ar kasar nan a matsayin wadda ta yi zarra a nahiyar Afirka la’akari da irin horon da jami’an ke samu ta fannoni daban-daban, inda ya yi fatan nan gaba za ta kere sa’a a duniya.

Tanko Muhammad ya bukaci ‘yan Jarida su taimakawa kokarinsa ta hanyar tona asirin masu cin hanci da rashawa a cikin hukumomin shari’a a ko ina su ke, kasancewar ba duka aka taru aka zama daya ba.

Babban Jojin ya ce kamar yadda a ke samun wasu ‘yan Najeriya da aikata laifukan cin hanci da rashawa, haka ma wasu alkalai ke aikata hakan, dalilin kenan da ya sa ya zama wajibi a bankado su.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!