Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Cin hanci da rashawa ne ke haifar da koma baya a Najeriya – Dr. Dukawa

Published

on

Masanin kimiyyar siyasa nan na jami’ar Bayero da ke nan Kano, Dakta Sa’idu Ahmad Dukawa ya bayyana cin hanci da rashawa a matsayin babban abinda ke haifar da koma-bayan al’amura a Najeriya.

Dakta Dukawa ya bayyana haka ne yau jim kadan bayan kammala shirin ‘Barka da Hantsi’ na nan tashar Freedom Rediyo da ya mayar da hankali kan matsalar dakatar da tsohon shugaban hukumar yaki da rashawa ta kasa, EFCC, Ibrahim Magu.

Ya bayar da shawarar daukar matakin gyara yadda hukumar ta EFCC ke gudanar da ayyukanta tare da sabunta dokokin da suka kafata don ba ta damar gudanar da ayyukan ta ba tare da yi mata katsalandan ba.

Wani dan kungiyar kwadago, Malam Isa Tijjani da ya kasance cikin shirin, cewa ya yi abu ne mai kyau idan shugaban kasa, Muhammad Buhari ya yi magana kan lamarin kasancewar shine ke da damar yin wani abu a kan matsalar don yi masa saiti.

Ya ce mafi yawan rigingimun da ake fama da su a kasar nan cin hanci da rashawa ne ke haddasa su.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!