Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Babbar kotun tarayya mai zamanta a Abuja ta bada belin Kanar Sambo Dasuki

Published

on

Babbar kotun tarayya mai zamanta a Abuja da bada belin tsohon mashawarcin shugaban kasa kan harkokin tsaro Kanar Sambo Dasuki mai ritaya.

Mai Shari’a Ijeoma Ojukwu ce ta zartas da wannan hukunci a safiyar yau Litinin, inda ta bayyana tsare shin da aka yi da cewa ba daidai bane, ya saba da tsarin doka da oda.

Wannan dai shi ne karo na shida da ake bada belin Sambo Dasuki kuma a kan kudi Naira miliyan N200M,sai dai jami’an tsaron sirri na DSS sun ki bin umarnin kotun wajen sakinsa.

Kotun dai ba bada umarnin wadanda za su tsaya masa su kasance suna mataki na 16 a aikin gwamnati, idan kuma ba ma’aikata ba ne su kasance suna gidaje a Maitama da Asokoro ko Utaku ko kuma Garki.

Kuma za su ajiye kudi Naira miliyan dari a asusun Kotun.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!