Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Gwamnatin jihar Lagos ta sanya dokar takaita zirga-zirgar manyan motoci

Published

on

Gwamnatin Jihar Lagos ta sanar da sanya dokar takaita zirga-zirgar manyan motocin dakon mai a fadin Jihar, tare da alkawarin ware musu da na su titin da za su rika bi.

Hakan dai ya biyo bayan mummunan hadarin da ya faru a gadar Otedola da ke kan hanyar Lagos zuwa Badin a ranar Alhamis din da ta gabata, wanda ya yi sanadiyyar asarar rayuka da dukiyoyin al’umma.

Kwamishinan Sufuri na Jihar Ladi Lawanson ne ya bayyana hakan a wani taron masu ruwa da tsaki da ya gudana wanda ya hadar da kungiyar masu dakon mai da iskar gas ta kasa NUPENG, da kungiyar direbobin tanka, da sauransu.

Haka zalika gwamnatin Jihar ta kuma ce duk wani direban tankar da zai shiga birnin wajibi ne ya nemi izini daga ma’aikatar Sufuri ta Jihar kwanaki 30 kafin shigowarsa

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!