Connect with us

Labarai

Babu zirga-zirgar ababen hawa a yankunan da za a yi zaɓe- CP Bakori

Published

on

Rundunar yan sandan jihar Kano ta tabbatar da cewar babu zirga-zirgar ababen hawa a kananan hukumomin Bagwai da Shanoni da kuma Ghari, tun daga karfe shida na safiyar Asabar zuwa uku na Yamma sakamakon zabukan cike gurbi na ‘yan majalisun dokokin jihar Kano da za a gabatar.

Kwamishinan yan sandan Kano Ibrahim Adamu Bakori ne ya bayyana hakan a zantawarsa da Freedom Radio, jim kadan bayan kammala taro na musamman da masu ruwa da tsaki kan zabukan da za a gabatar.

Kwamishina Ibrahim Adamu Bakori, ya kuma ja kunnen duk wanda yasan ba zabe zai ba daya guji zuwa yankunan da za a gudanar da zabukan dan kuwa idan suka kama mutum doka za tai aiki a kansa.

Da ya ke nasa jawabi, shugaban hukumar zabe ta kasa INEC reshen Jihar Kano Ambassador Abdu A Zango ya ce, sun shirya tsaf dan gudanar da zabukan.

A ranar Asabar mai zuwa ne dai za a gudanar da zabukan cike gurbin a kananan hukumomin Bagwai da Shanono da kuma karamar hukumar Gari.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!