Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Badaƙalar Naira Biliyan 31: ICPC tana neman surikin Buhari ruwa a jallo

Published

on

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta ƙasa (ICPC) ta bayyana ɗaya daga cikin surukan shugaban ƙasa Muhammadu Buhari Gimba Ya’u Kumo a matsayin wanda take nema ruwa a jallo sakamakon zargin sa da hannu a badaƙalar dala miliyan sittin da biyar kwatankwacin naira biliyan talatin da ɗaya.

 

Kumo wanda ya auri ɗaya daga cikin ƴayan shugaba Buhari (Fatima) a shekarar 2016 ana zargin sa ne tare da wasu mutane biyu da suka hada da: Tarry Yusuf da kuma Bola Ogunsola da almundahanar kudaden.

 

A cikin wata sanarwa da hukumar ta ICPC ta fitar mai dauke da sa hannun mai magana da yawunta Azuka Ogugua, ta yi shelar cewa duk wanda ya san inda surikin shugaban kasar ya ke da ya gaggauta sanar da ita ko kuma ofishin ƴan sanda da ke kusa.

 

Shidai Gimba Umar Kumo ya rike muƙamin shugaban bankin samar da gidaje ta ƙasa (Federal Mortgage Bank of Nigeria) a lokacin mulkin Goodluck Jonathan.

 

Ana dai zargin surikin shugaban kasar ne shi da mutanen biyu da karkatar da kudaden hukumar samar da gidaje ta ƙasa da suka kai dala miliyan sittin da biyar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!