Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Badaru ya bada umarnin bude makarantun boko 40

Published

on

Gwamnan jihar Jigawa Mohammed Badaru Abubakar ya ce za’a bude makarantu 40 a jihar ya yin da bada umarnin dukkanin ma’aikatan jihar su koma bakin aiki daga rana 4 ga watan da muke ciki.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ya yin da yake ganawa da manema labarai a birnin Dutse yana mai baiwa ma’aikatun ilimi da lafiya umarnin su fito da tsare-tsaren su wanda zai sanya kada a take dokokin cutar COVID- 19.

A dai kwanakin baya ne gwamnan ya bada umarnin ma’aikata dake mataki na 12 su koma bakin aiki.

A ranar 24 ga watan Maris ne gwamnatin jihar ta bada umarnin ma’aikatan su yi aiki daga gida don kare kan su daga cutar Corona.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!