Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Da dumi –dumi : Ganduje zai bude makarantun boko a Kano

Published

on

Gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya amince da a bude makarantun boko a ranar 10 ga watan Agusta don rubuta jarrabawar kammala sakandire a sassan jihar nan a bana.

Kwamishinan ilimi na jihar Muhammad Sanusi Kiru ya sanar da hakan a taron manema labarai da aka yi a yau Litinin.

Muhammad Sanusi Kiru ya umarci dukkanin shugabannin makarantu su tsara wajen karbar dalibai dake makarantun kwana a ranar 9 ga wannan watan na Agusta, don fara karatu gadan-gadan.

A dai watan Maris ne gwamnatin jihar Kano ta garkame makarantun jihar don kare dalibai daga kamu daga cutar COVID -19.

 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!