Labarai
Da dumi –dumi : Ganduje zai bude makarantun boko a Kano
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2020/06/Ganduje-3-1280x720-1.png)
Gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya amince da a bude makarantun boko a ranar 10 ga watan Agusta don rubuta jarrabawar kammala sakandire a sassan jihar nan a bana.
Kwamishinan ilimi na jihar Muhammad Sanusi Kiru ya sanar da hakan a taron manema labarai da aka yi a yau Litinin.
Muhammad Sanusi Kiru ya umarci dukkanin shugabannin makarantu su tsara wajen karbar dalibai dake makarantun kwana a ranar 9 ga wannan watan na Agusta, don fara karatu gadan-gadan.
A dai watan Maris ne gwamnatin jihar Kano ta garkame makarantun jihar don kare dalibai daga kamu daga cutar COVID -19.
You must be logged in to post a comment Login