Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ban koma gida na ɓuya ba- Muhammadu Bazoum

Published

on

Al’ummar Jamhuriyyar Nijar na ci gaba da bayyana ra’ayoyin su game da raɗe-raɗen da ake yi na cewa shugaban ƙasar Bazoum ya ƙauracewa kwana a fadar gwamnatinsa, saboda tsoron juyin mulki dake faruwa a wasu ƙasashen na yammacin Afurka.

Wannan lamari dai yasa ƴan adawa da gwamnatin ke cewa dama Bazoum kwatar mulki yayi ba zaɓarsa talakawa suka yi ba.

Da yake martani game wanna batu, kakakin Jam’iyya PNDS Tarayya Alhaji Asmana Muhammadu yace wannan lamari ba haka yake ba, “Shugaban ƙasa baya tsoron kowa, ni na sanshi sakarata 30 tare da shi, bayan Allah babu wanda yake tsoro tun da ma, ballentana yanzu da ya zama shugaban ƙasa”.

Ce-ce kucen dai ya samo asaline bayan da wata jarida ta ƙasar Kanada ta wallafa cewa, shugaban ƙasar Nijar Muhammadu Bazoum ya ƙauracewa kwana a gidan Gwamnati, tun lokacin da sojoji suka kifar da Gwamnatin ƙasar Burkina Faso.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!