Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Bankin CBN ya sanya ranar da masu POS za su kammala Rijistar Kamfanoni ta CAC

Published

on

Babban Bankin Najeriya (CBN) ya bayar da wa’adin ranar 7 ga Yuli, 2024 ga masu POS su kammala rajista da Hukumar rajistar kamfanoni ta ƙasar (CAC).

An bayyana hakan ne lokacin da aka yi wata ganawa tsakanin kamfanonin hada-hadar kuɗi na ƙasar da shugaban hukumar ta rajistar kamfanoni, Hussaini Magaji a Abuja ranar Talata.

Da yake jawabi a wurin taron, shugaban na CAC ya ce wa’adin watanni biyu na yin rajistar ya yi “daidai da ka’idojin doka da kuma umarnin babban bankin Najeriya”.

Wata sanarwa da CAC ta fitar kuma ta kara da cewa “An ɗauki matakin ne domin kare masu mu’amala da kamfanonin hada-hadar kuɗi tare kuma da ƙarfafa tattalin arziƙi.”

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!