Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Bankin duniya zai baiwa Kano da wasu jihohi bashin kudi

Published

on

Bankin Duniya zai bai wa jihar Kano da wasu jihohin kasar nan guda shida bashin kudi da ya kai dala miliyan dari biyar domin bunkasa harkokin karatun ‘ya’ya mata.

A cewar bankin na Duniya rancen wanda babu kudin ruwa a cikinsa, za ayi amfani da shine wajen bunkasa karatun mata a matakan sakandire a jihohin guda bakwai.

Hakan na cikin wata sanarwar ce da bankin na Duniya ya fitar yau a Abuja wanda ke cewa, kudin wani bangare ne na ,kudaden da bankin ke bai wa kasashe masu tasowa don gudanar da ayyukan raya kasa.

Jihohin da za su amfana da bashin na bankin Duniya don bunkasa karatun ilimi mata sun hada da: Kano da Kebbi da Kaduna da Katsina da Borno da Plateau da kuma Ekiti

Haka zalika sanarwar ta kara da cewa, kudaden za su kuma taimaka wajen koyar da sana’oin dogaro da kai ga mata da kuma wayar da kan mata kan harkokin kiwon lafiya da sauransu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!