Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Majlisar Kano ta musanta zartar da dokar dandatsa

Published

on

Majalisar dokokin jihar Kano ta musanta cewa ta zartar da dokar yin dandatsa ga mutanen da aka kamasu da laifin fyade.

Dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Dala Lawan Husaini Chediyar ‘Yan-Gurasa ne ya bayyana haka yayin zantawa da tashar freedom rediyo.

Ya ce, an dai gabatar da kudirin gaban majalisar a kwanakin baya, sannan sai anji ra’ayin al’umma kafin a dauki mataki kan lamarin.

Ya kuma ce, majalisar za ta tsats-tsefe kudirin sosai kafin amince da shi.

Dan Majalisar ya kara da cewa masu ruwa da tsaki da suka hada da malamai da sarakuna za su taka rawa wajen tabbatar da wannnan doka .

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!