Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Basketball: zamu lashe gasar Afrobasket da za’ai a kasar Ruwanda-Mike Brown

Published

on

Mai horas da ‘yan wasan kwallon Kwando na Najeriya, D’TIGERS, Mike Brown, ya ce yana fatan Najeriya za ta lashe gasar cin kofin kwallon  Kwando ta Afrobasket ta bana.

A yau ne dai 24 ga watan Agustan da muke ciki za’a fara gudanar da gasar ta wannan shekara, inda za’a karkareta a ranar 5 ga watan Satumba mai kamawa.

Za dai a gudanar da gasar a babban filin wasa na Kigali dake kasar Ruwanda.

Najeriya na cikin rukunin C da kasar Mali da Kenya da kuma kasar Ivory Coast.

A gobe laraba dai 25 ga watan na Augusta Najeriya za ta fafata da kasar Mali a wasan farko da zatai na rukuni kafin daga bisani ta kara da kasar Kenya da kuma Ivory Coast.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!