Labaran Wasanni
Basketball: zamu lashe gasar Afrobasket da za’ai a kasar Ruwanda-Mike Brown
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2021/08/127269273_2797726453808276_4560983890071650817_o.jpg)
Mai horas da ‘yan wasan kwallon Kwando na Najeriya, D’TIGERS, Mike Brown, ya ce yana fatan Najeriya za ta lashe gasar cin kofin kwallon Kwando ta Afrobasket ta bana.
A yau ne dai 24 ga watan Agustan da muke ciki za’a fara gudanar da gasar ta wannan shekara, inda za’a karkareta a ranar 5 ga watan Satumba mai kamawa.
Za dai a gudanar da gasar a babban filin wasa na Kigali dake kasar Ruwanda.
Najeriya na cikin rukunin C da kasar Mali da Kenya da kuma kasar Ivory Coast.
A gobe laraba dai 25 ga watan na Augusta Najeriya za ta fafata da kasar Mali a wasan farko da zatai na rukuni kafin daga bisani ta kara da kasar Kenya da kuma Ivory Coast.
You must be logged in to post a comment Login