Labarai
Bayan doke Madrid Arsenal za ta kara da Paris St Germain

Bayan ta doke ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Real Madrid, Arsenal za ta kara da ƙungiyar Paris St Germain gida da waje a zagayen daf da karshe a gasar Champions League.
A daren jiya Laraba ne kungiyar ta Arsenal ta yi fitar da Real Madrid daga Champions League Bayan da ta doke ta da ci 2-1 har gida.
Wannan nasara ce kuma ta bai wa Arsenal damar kaiwa ga zagayen daf da karshe.
Idan za a iya tunawa, a makon jiya ne Arsenal ta doke Real Madrid da ci 3-0 a filin wasa na Emirates da ke birnin London.
You must be logged in to post a comment Login