Connect with us

Labarai

Bazoum ya jinjinawa hukumar wanazar da zaman lafiya bisa gudunmawa da ta ke bayar a ƙasar ta Nijar

Published

on

Hukumar Haute Autorité pour la Consolidation de la Paix mai wanzar da zaman lafiya ta Nijar, ta gudanar wani taro da wakilan ƙabilun jihohin Agadas da Tawa.

Taron da ya mayar da hanakali kan yadda suka taka rawa wajen tabbatar da zaman lafiya a yankin da a baya ya fuskanci rikicin ƴan tawaye.
Shugaban ƙasar Bazoum Mohammed ne ya jagoranci zaman a garin Ingal na jihar ta Agadas.

Da ya ke jawabi yayin taron shugaban hukumar Janar Abu Tarka, ya ce sun shirya wannan taron ga ‘yan tawayen da suka tuba don kara tabbatar da tsaro a yankunan.

Bayan sauraran jawabai daga shugabannin yankunan Shugaban kasa Bazoum, ya jinjina musu bisa kokarin da suke na wanzar da zaman lafiya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!