Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Bill Clinton zai halarci taron sanya hannun yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin ‘yan ’takarar Najeriya

Published

on

Kwamitin wanzar da zaman lafiya tsakanin ‘yan takarar Najeriya, ya ce ana saran  tsohon Shugaban kasar Amurka Bill Clinton zai halarci taron  sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin ‘yan ’takarar shugabancin kasar nan karkashin inuwar jama’iyar APC, Muhammadu Buhari da kuma takwaransa na jam’iyyyar PDP Alhaji Atiku Abubakar.

Cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun babban sakataren kwamitin wanzar da zaman lafiyar, Atta Barkindo, ya ce, taron zai gudana ne a jibi laraba a babban dakin taro na kasa da kasa da ke birin tarayya Abuja.

Ya kuma ce, babban sakatariyar kungiyar kasashen rainon Ingila, Baroness Patricia Scotland, za ta halarci taron, a inda bayan kammala taron sanya hannu kan yarjijeniyar zaman lafiyar, Bill Clinton zai gana da yan’takarar jami’yyun guda biyu.

Atta Barkindo, ya kara da cewa, a yayin babban zaben Najeriya da ke karatowa ya zama wajibi al’umma su san mahimmancin zaman lafiya a tsakaninsu, tare da kauracewa rigingimu a tsakanin matasan kasar nan musamman a lokacin zabe da kuma bayan zaben.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!