Connect with us

Labarai

Borno: An yi jana’izar Yan Sanda 4 da suka rasu sakamakon harin ƴan taʼadda

Published

on

Rundunar Yan Sandan jihar Borno ta yi jana’izar jami’anta hudu da suka rasu a wani harin da ƴan taʼadda suka kai a karamar hukumar Nganzai.

   

Rundunar, ta bayyana hakan ne ta cikin sanarwar da jami’inta na hulda da jama’a ASP Nahum Kenneth Daso ya fitar.

 

Sanarwar ta bayyana sunayen jami’an da suka rasu da suka hada da Insifekta Samuel Ezekiel, Insifekta Sanusi Mohammed, sai kuma Constable Bitrus Luka da Constable Shaibu Bukar.

 

Sanarwar ta nuna cewa an gudanar da jana’izar ne a makabartar Kawar Maila da kuma makabartar gidan yari da ke Maiduguri.

 

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Borno, Naziru Abdulmajid tare da wasu manyan jami’ai sun halarci jana’izar.

 

An gudanar da addu’o’i ga mamatan karkashin jagorancin limamin rundunar, CSP Bukar M. Gajibo da kuma Fasto CSP Theophilus Mutum.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!