Connect with us

Labarai

Borno: Mutane 5 sun rasu sakamakon rushewar gini

Published

on

Aƙalla mutane biyar ne suka rasu, ciki har da wata uwa da yara huɗu bayan rushewar wani gini a jihar Borno.

 

Rahotonni sun bayyana cewa, lamarin ya faru ne a unguwar Binta Suga da ke birnin na Maiduguri, inda ya jefa mazauna yankin cikin jimami.

 

Wani mazaunin unguwar Babagana Usman ya shaida wa BBC cewa ginin ba shi da wani lahani kafin ruftawarsa.

 

Ya ƙara da cewa an gudanar da jana’izar mamatan a Litinin din makon nan.

 

Sai dai har zuwa lokacin fitar rahoton, hukumomin yankin ba su ce komai ba a kan wannan batu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!