Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Jihohi sha biyar za su sami tallafin ilimi daga Global Partnership For Education – Buhari

Published

on

Hukumar kula da tatalin arziki ta kasa ta ce jihohi sha biyar a kasar nan za su samu tallafin ilimi daga wata kungiyar tallafawa ilimi mai suna Global Partnership For Education a wani mataki na magance matsalar da annobar corona ta yiwa bangaren ilimi.

Gwamnan jihar Kaduna Malam Nasir El-rufa’I ne ya bayyana haka lokacin taron kwamitin wanda mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo ya jagoranta.

An gudanar da taron ne ta kafar Internet a fadar shugaba kasa da ke Villa a Abuja.

Nasir El-rufa’I ya ce jihohin da za su samu tallafin sune jihar Abia, Anambra, Akwa Ibom, Benue, Ebonyi, Jigawa.

Sauran sun hadar:- jihar Kaduna, Katsina, Kebbi, Kano, Nassarawa, Niger, Plateau, Sokoto da kumad Zamfara.

Yace, ma’aikatar ilimi ta tarayya ta gabatawra da hukumar wasu ka’idoji da za a bi ta yadda daliban za su ci gaba da karatu a wannan yanayi na corona.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!