Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

ilimi

Tsaro: Muna ci gaba da kwashe ɗaliban mu daga Jos – El-rufa’i

Published

on

Gwamnatin jihar Kaduna ta ce, ta fara kwaso ɗalibai ƴan asalin jihar da ke karatu a jami’ar Jos da sauran kwalejojin ta zuwa gida.

Shugaban hukumar bada tallafin karatu a jihar Malam Hassan Rilwan  ne ya bayyana hakan a Alhamis ɗin nan, ta cikin wata sanarwa da ya fitar.

Ya ce, kwaso ɗaliban ya biyo bayan yadda jihar ke ci gaba da fuskantar matsalaolin tsaro a kwanakin nan, wanda kuma tuni gwamnatin jihar ta bada umarnin a fara kwaso su zuwa gida.

Malam Hassan Rilwan ya kuma ce, tun a ranar Juma’ar da ta gabata ne aka fara jigilar ɗaliban daga Jos zuwa jihar Kaduna, kuma za a kammala aikin a ƙarshen makon da muke ciki.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!