Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Buhari ya aikewa majalisa ƙudurin ƙarin kasafin kuɗi na 2022

Published

on

Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya mikawa majalisar dokokin Najeriya ƙarin kudirin kasafin kuɗi na naira tiriliyan 2 da biliyan 55 domin amincewa.

Kazalika shugaba Buhari na neman a sake duba dokar kasafi ta 2022 domin samun ƙarin kasafin kuɗin tallafin man fetur daga watan Yuni zuwa Disambar 2022.

Buƙatar hakan na cikin wata wasiƙa da aka aikawa shugaban majalisar dattawa Ahmad Lawan da shugaban majalisar wakilai Femi Gbajabiamila a ranar Talata.

Buhari zai tafi ƙasar Belgium

Buhari ya kuma buƙaci majalisar dokokin ƙasar ta dawo da wasu ayyukan da majalisar ta cire tun da farko a cikin kasafin kuɗin 2022.

Idan za a iya tunawa dai tun da fari Buhari ya koka kan sauyin da ƴan majalisar suka yi a cikin ƙudirin kasafin kuɗin shekarar 2022 na Naira tiriliyan 17 da biliyan 126 da ya sanyawa hannu a cikin watan Disamba.

Sai dai majalisar ta amince da Naira tiriliyan 17 da biliyan 1 saɓanin Naira tiriliyan 16 da biliyan 3 da ya gabatar a watan Oktoba, inda ya ƙara kusan Naira biliyan ɗari 700 a cikin kasafin kuɗin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!