Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Addini

Buhari ya jinjinawa sojojin da ke yaki da boko haram

Published

on

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yabawa dakarun operation lafiya dole da ke aikin samar da tsaro a yankin arewa maso gabashin kasar nan.

 

Muhammadu Buhari wanda ministan tsaro manjo janar Bashir Salihi Magashi mai ritaya ya wakilta, ya bayyana hakan ne yayin wata ziyara da ya kai shalkwatar dakarun operation lafiya dole da ke garin Maiduguri a jihar Borno.

 

Muhammadu Buhari ya kuma ce, ba ko shakka dakarun na operation lafiya dole suna iya kokarinsu wajen ganin sun kakkabe ‘yan ta’addar boko haram a fadin kasar nan.

 

Inda ya shaidawa sojojin da suka jikkata a bakin daga da kuma iyalan wadanda suka rasa rayukansu da cewa, gwamnati za ta ci gaba da kula da halin da suke ciki don rage musu radadin halin da suka shiga sakamakon sadaukar da rayukansu wajen kare rayuka da dukiyoyin al’ummar NAJERIYA.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!