Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Buhari ya kara sama da Naira Biliyan 600 a aikin titin Kano zuwa Abuja

Published

on

Majalisar zartarwa ta kasa (FEC) a jiya laraba ta amince da sake fasalta aikin titin Kano zuwa Abuja.

Majalisar ta ce a yanzu za a kashe Naira Biliyan dari bakwai da casa’in da bakwai da miliyan dari biyu ne wajen gudanar da aikin.

Wannan dai na nuna cewa an samu karin Naira Biliyan dari shida da arba’in da biyu da miliyan dari biyu akan yadda aka tsara za a gudanar da aikin tun farko, a baya dai an tsara za a gudanar da aikin ne akan Naira Biliyan dari da hamsin da biyar.

Ministan ayyuka da gidaje Babatunde Raji Fashola ne ya bayyana haka ga manema labarai a jiya laraba jim kadan bayan kammala taron majalisar zartarwa ta kasa.

A cewar ministan tun farko an tsara aikin kwaskwariman titin ne akan kudi naira biliyan dari da hamsin da biyar ga kamfanin Julius Berger.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!