Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Buhari ya kare Emefiele akan sake fasalin Naira

Published

on

Tsohon Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari yayi kakkausar suka ya kare matakin sauya fasalin Naira da babban bankin Najeriya ya yi gabanin Zaɓukan 2023, inda ya ce manufar ta bai wa kasar abin da ake kira ‘tsaftataccen zabe.

Matsayin Buhari na kunshe ne a cikin wani sabon littafi mai suna: Aiki tare da Buhari: Reflections of a Special Adviser, Media and Publicity (2015-2023), wanda Shugaba Bola Tinubu ya bayyana a Abuja A Ranar Talata.

A cikin littafin, Buhari ya yi karin haske kan batun sake fasalin Naira da kuma dalilin da ya sa bai kori tsohon Gwamnan CBN, Godwin Emefiele ba, a lokacin da fastocinsa na neman shugabancin Najeriya suka ci karo da kasar a jiki da kuma kafafen yada labarai.

Buhari ya ce ba daidai ba ne ya kori Emefiele tun da bai sanar da shi ko daya daga cikin mukarrabansa ba cewa ya tsaya takarar Shugabancin kasar a 2023.

Tsohon Shugaban kasar ya kuma bayyana karara cewa karancin Naira da ake ta fama da shi har ya zuwa yau, ba da gangan aka yi don hukunta ‘yan Najeriya ba, kamar yadda wasu ke zagon kasa.

Buhari ya ce: “Ba da gangan aka yi karancin kudi don hukunta ’yan Najeriya ba, Dimokuradiyya ta bai wa mutane damar bayyana ra’ayinsu, Kuma ba mu yi yunkurin tunkarar su ba. Mutane sun fahimci abubuwan da suka zaɓa, kuma ba mu tilasta su ba.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!