Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Buhari ya nemi sahalewar majalisar wakilai kan karin kasafin kudi

Published

on

Gwamnatin tarayya ta aikewa da majalisar wakilai karin kasafin kudi da za a kashe wajen samar da allurar rigakafin COVID-19 ga al’ummar kasar nan.

Ministar Kudi Kasafi da Tsare-tsare Hajiya Zainab Ahmed ce ta bayyana hakan a yau Alhamis, ta na mai cewa za a shirya daftarin kasafin kudin a watan Maris mai kamawa.

Ahmed tayi magana ne a jawabin farko na sanarwa da aka gabatar a Fadar Shugaban Kasa dake Abuja.

“Karin kasafin kudi, na farko zai kasance a watan Maris game da annobar COVID-19 amma kuma za mu yi bitar tsakiyar shekara kamar yadda muka yi a bara na kasafin kudin.”

“Idan a lokacin muna yin bitar kuma akwai bukatar komawa don yin duk wani gyara na karin kasafin kudi, a wancan lokacin, za mu dauki wannan shawarar; idan ba haka ba, za mu kawo rahoton bita kawai,” inji ta.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!