Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Buhari ya rage farashin man fetur

Published

on

Gwamnatin tarayya ta sanar da rage farashin man Fetur daga naira 145 zuwa naira 125, biyo-bayan karyewar farashin man a kasuwar duniya a dalilin bullar kwayar cutar Corona.

Kamfanin mai na kasa NNPC ne ya sanar da hakan a shafinsa na twitter, inda ya umarci gidajen man da su fara sayarwa a kan wannan farashi na naira 125 daga gobe alhamis.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ne ya amince da zaftare farashin bayan da karamin ministan man Fetur din kasar nan Timipre Sylva ya gabatarwa majalisar zartarwa ta tarayya rahoto a kai.

Rahotanni daga fadar shugaban kasa sun bayyana cewa Mr Timipre Sylva ne ya bukaci a rage farashin, a dalilin faduwar farashin na sa a kasuwar duniya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!