Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Covid-19: Za a rufe makarantu a jihohin Arewa masu yamma

Published

on

Gwamnonin yankin Arewa maso Yamma sun ce za su rufe daukacin makarantun dake yankin daga ranar Litinin mai zuwa, saboda annobar cutar Coronavirus.

Shugaban kungiyar Gwamnonin yankin Arewa maso yamma, Gwamnan jihar Katsina Aminu Bello Masari ne ya bayyana hakan, ta bakin Gwamna Atiku Bagudu na jihar Kebbi wanda ya yi jawabi a madadinsa, yayin wani taro da gwamnonin suka gudanar a jihar Kaduna.

Wakilin mu a Kaduna Babangida Aliyu Abdullahi ya rawaito mana cewa gwamnonin sun yi taron ne a fadar gwamantin jihar Kaduna a yau Laraba.

Karin labarai:

COVID-19 : Tambuwal ya dakatar da bajakolin nuna al’adu

Kano: Babu rahoton bullar cutar COVID-19 -Dr, Aminu Tsanyawa

Taron ya samu halartar Gwamnonin jihohin Katsina, da Kebbi, da Kaduna, da jihar Jigawa, da Zamfara, sai kuma jihohin Sokoto, da Niger.

Mataimakin Gwamnan jihar Kano Nasiru Yusuf Gawuna shine ya wakilce gwamnan Kano a taron.

Sai Gwamnan jihar Kwara dake yankin arewa ta tsakiya wanda ya bugo waya yace sun aminta da duk matakin da Gwamnonin yankin arewa maso yamma suka dauka, kasancewar shugaban Gwamnonin arewa ta tsakiya wato Gwamnan jihar Niger Muhammafd Sani Bello ya halarci wannan taro.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!