Labarai
BUK ta sanya ranar Jarabawar Post UTME
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2021/03/bayero-university.jpg)
Jami’ar Bayero da ke Kano ta sanar da ranakun Alhamis, juma’a da kuma Asabar,18, 19, 20 ga watan da muke ciki na Maris a matsayin ranakun da za a gudanar da jarabawar gwaji na dalibai da ke neman gurbin karatu a jami’ar wadanda suka rubuta jarabawar JAMB wato Post UTME.
Hakan na cikin wata sanarwa ce da jami’ar ta fitar a jiya juma’a.
A cewar jami’ar, shafin website da za ayi rajistar jarabawar ta gwaji wato Aptitude Test za a rufeshi da karfe goma sha biyu na daren juma’a sha biyu ga wannan wata.
Saboda haka jami’ar ta bukaci dalibai da ke neman gurbi a jami’ar da su tabbata sun cire takardar shaidar shiga ajin rubuta jarabawar wato examination slip tsakanin ranakun Alhamis zuwa sha biyar ga watan Maris.
Sai dai jami’ar ta ce, za a iya ci gaba da fitar da takardar ta slip wato shaidar shiga ajin rubuta jarabawar har zuwa ranar Laraba 17 ga wata.
You must be logged in to post a comment Login