Labaran Wasanni
CAF: Enyimba ce za ta lashe gasar – Fatai Osho
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2021/02/enyimba-more-latest-lineup-1140.jpg)
Mai horas da kungiyar kwallon kaga Enyimba, Fatai Osho, ya ce, yana da kwarin gwiwar kungiyar za ta zama kungiya ta farko a Najeriya da za ta lashe gasar cin kofin kalubala ta kungiyoyin Afrika.
A yanzu haka dai kungiyar tana kan a rukunin A tare da Orlando Pirates a Afrika ta kudu da Entente Sportive Setif dake Algeria da kuma Al Ahli Benghazi a Libya.
Enyimba dai ta samu fitowa ne yayin da ta doke Rivers United a bugun daga kai sai mai tsaron raga bayan sunyi canjaras da ci 1-1.
A kuma ranar goma ga watan Maris mai zuwa ne kungiyar za ta karbi bakuncin Ahli Benghazi daga kasar Libya.
You must be logged in to post a comment Login