Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

CBN ya ceto kasar nan daga yunwa ana tsaka da COVID -19 – Godwin Emefiele

Published

on

Central Bank Of Nigeria

Babban bankin kasa CBN ya ce, ya ceto kasar nan daga karancin abinci da barazanar fadawa yunwa a yayin da ake tsaka da fama da annobar Covid-19.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da daraktan yada labarai na bankin Isaac Okorafor ya fitar, inda ya ce babban bankin kasa ya musanta batun kwamitin tattalin arziki da ya ce bankin ya gaza wajen tabbatar da ingancin shirye-shiryen samar da abinci da fitar da jama’ar kasar nan daga matsanancin talauci.

A ranar litinin din da ta gabata ne kwamitin tattalin arziki na kasa ya ce an sami wawakeken gibi a batun samar da abinci da kare al’ummar kasar nan daga fadawa halin yunwa, duk kuwa da makudan kudaden da babban bankin kasa CBN ya ware don yin hakan.

Sai dai ko da bankin ke mayar da martani kan zargin, ya ce yana iya bakin kokarin sa wajen ganin an yi amfani da kudaden da ya ware wajen samar da abinci da kuma rage radadin talauci.

Bankin bai tsaya iya nan ba, sai da ya bada misali kan yadda al’ummar kasar nan dubu 103 da dari 189 suka amfana da tsabar kudi naira biliyan 59 da miliyan 12 don rage musu radadi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!