Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Yawanci yara ‘yan arewacin kasar nan ne ke bata – RED CROSS

Published

on

Kungiyar bayar da Agaji ta RED CROSS ta ce akalla mutane dubu 23 mafi yawancin su yara ne suka bata a Najeriya musamman a yankin arewacin kasar nan.

Ta cikin wani rahoto da kungiyar ta fitar ta bayyana cewa mafi yawan mutanen da suka batan, sun bata ne sakamakon rikicin Mayakan Boko Haram.

Sai dai kuma kungiyar ta RED CROSS ta bayyana takaicin ta kan yadda ta ce annobar Covid-19 na dakile aikin neman mutanen da suka batan da kuma hada su da iyalan su.

A cewar Rahoton, a Nahiyar Africa akalla mutane dubu 44 ne aka tabbatar da batun batan su sakamakon rikice-rikice da kuma sauyin yanayi da ke tilastawa jama’a yin gudun hijira.

Kungiyar ta kuma ce cikin wannan adadi kaso 45 yara ne, kuma kasashen Nigeria, Ethiophia, Sudan ta kudu, kamaru, Libya, Somalia, da jamhuriyar Dimokradiyyar Congo ne ke da kaso 82 cikin dari na wadanda aka tabbatar da batan su.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!