Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Cin hanci da rashawa: Haƙƙin kowa ne ya yaƙi matsalar da kansa – Barista Balarabe

Published

on

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa a Kano ta ce, haƙƙin kowa ne ya yaƙi matsalar cin hanci da rashawa a duk inda yake.

Shugaban hukumar Barista Mahmud Balarabe ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis yayin wani tattaki da hukumar ta shirya a wani ɓangare na bikin ranar yaƙi da cin hanci da rashawa ta duniya.

Barista Mahmud ya ce, daƙile matsalar cin hanci da rashawa a ko’ina a faɗin duniya na samun nasara ne idan aka samu haɗin kan al’umma.

“A Kano Muna s nasarar yaƙi da matsalar cin hanci da rashawa, domin kuwa idan aka kwatanta da shekarar bara za a ga an samu rahuwar matsalar”.

Ya ce “Maƙasudin shirya irin wannan tattaki shi ne ƙara janyo hankalin al’umma kan sanin muhimmancin ranar da kuma kira a kan su zama jakadun yaƙi da cin hanci da rashawa a kowane mataki”.

Majalisar ɗinkin duniya ce ta ware duk ranar 9 ga watan Disambar kowacce shekara matsayin ranar yaƙi da cin hanci da rashawa da nufin nusashshe da al’umma illolin da cin hanci ke da shi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!