Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Coronavirus ta kama ‘yan kwamitin yaki da cutar a Kano

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano ta tabbatar da cewa shugaban Kwamitin kar ta kwana na yaki da cutar Covid-19 na Jihar Kano Farfesa Abdulrazak Garba tare da wasu mambobin kwamitin guda 3 sun kamu da cutar Corona.

Kwamishinan lafiya na Jihar Kano Dr Aminu Ibrahim Tsanyawa ne ya tabbatar da hakan ta cikin wata sanarwa da jami’in yada labaran ma’aikatar Hadiza Namadi ta fitar yau.

Ta cikin sanarwar kwamishinan ya shawarci jama’a da kaucewa cakuduwa da juna sannan kuma su zauna a gidajensu, kuma gwamnatin Jihar Kano tana ci gaba da daukar matakan dakile yaduwar cutar.

Kafin zuwan wannan rahoto dai mutane 21 ne aka sanar daewa sun kamu da cutar tare da mutuwar mutum guda.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!