Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Cudanya da Hausawa ne ya sa na iya Hausa a Saudiyya- Dan Bangladesh

Published

on

Wani dan kasar Bangladash mazaunin kasar Saudiyyya mai suna Muhyuddin yace bai taba zuwa kasar Hausa ba, amma zaman sa a birnin Makkah na kasar Saudiyya ne da cudanya da al’ummar Hausawa yasa ya iya harshen Hausa,

Muhiyyuddin ya fadi hakan ne a wata tattaunawa da yayi da yan Najeriya mazauna kasar Saudiyya.

Akwai wata unguwa a brining Makkah da ake kira da dogon gida wadanda al’ummar Hausawa da dama ke zaune a yankin .

Muhiyyudin yace bai taba zuwa Najeriya ba ko jamhuriyar Nijar ,amma cudanya da Hausawa ne a dogon gida yasa ya iya harshen Hausa.

Mutumin dan kasar ta Bangladesh ya kara da cewa a hankali ya rika kokarin koyan harshen na Hausa.

Yace bait aba cin abincin Hausawa ba amma ya taba cin tsire .

Muhuyyiddin yace sanaarsa a kasar ta Saudiyya itace sayar da jallabiyya kuma nan gaba yana muradin ya zo Najeriya da niyyar ziyartar wasu jihohi.

Saurari cikakkiyar tattaunawar da akayi dashi:

https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2019/09/Abbas-Yushau.mp3?_=1

Ayi sauraro lafiya.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!