Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Cutar Sankarau ta kashe yara 60 a Kebbi

Published

on

Yayin da cutar Sankarau ke ci gaba da yaduwa cikin gaggawa a wasu daga cikin hohin Arewacin kasar nan, rahotonni sun tabbatar da mutuwar yara 60 a kananan hukumomin Gwandu da Jega da kuma Aliero na jihar Kebbi.

Wannan dai na zuwa ne bayan da kungiyar bayar da agaji a fannin lafiya ta Medecins Sans Frontieres MSF da aka fi sani da Doctors Without Borders ke ci gaba da yin gargadin daukar matakan kare kai daga kamuwa da cutar.

Haka kuma kungiyar, ta bukaci da a dauki matakin gaggawa wajen dakile yaduwar cutar wadda zuwa yanzu fiye da mutane 500 suka kamu da ita a yankunan Gwandu da Jega da kuma Aliero.

A cewar wani Likita da ke aiki da kungiyar Dakta Bukar Galtimari, akwai bukatar a rika yin gaggawar kai wadanda suka kamu da cutar asibiti domin ceton lafiyarsu kasancewarta cuta mai matukar hatsari.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!