Connect with us

Labarai

Da ɗumi-ɗumi: Majalisar wakilai ta yi sammacin ƙungiyar ASUU da wasu ministoci

Published

on

Majalisar wakilai ta ƙasa ta yi sammacin wasu ministoci biyu da shugaban ƙungiyar ASUU.

Kakakin majalisar Femi Gbajabiamila ne ya bada umarnin sammacin.

Ministocin da aka yi sammacin su sun haɗa da ministar kuɗi kasafi da tsare-tsare Zainab Ahmed da ministan Ilimi Adamu Adamu.

Majalisar ta kuma yi sammacin shugaban ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta ƙasa Farfesa Emmanuel Osedeke.

Majalisar ta buƙaci dukkanin su da su gurfana a gabanta a ranar Alhamis 18 ga Nuwamban 2021 yayin zaman majalisar.

 

PUNCH

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!