Connect with us

Labarai

Da Dumi-dumi: Hisbah ta hana jin wakar Hamisu Breaker

Published

on

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta sanar da hana sauraron wata sabuwar Wakar Hamisu Breaker mai suna Amanata.

Mataimakiyar Babban Kwamandan hukumar ta Hisbah a ɓangaren Mata Dakta Khadija Sagir, ce ta bayyana hakan ta cikin wani sakon murya da ta aiko wa Freedom Radio a yau Alhamis.

Dakta Khadija Sagir ta ce, waƙar ƙarara ta na nuna zina tare da nuna cewa mai yinta ya na cikin halin maye.

Ta kuma ce, sun gano faya-fayan bidiyo da suke nuna yadda mata ke daukar bidiyo suna bin wakar tare da yin lanƙwashe-lanƙwashe da karya murya.

Haka kuma hukumar ta yi kira ga matasa su ƙaurace wa sauraron waƙar ta Amanata wadda mawakin Hamisu Breaker , ya rera, don kuwa a wajen hukumar sauraron wannan waƙa haramun ne.

Latsa Alamar Play domin jin muryarta

https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2025/04/WhatsApp-Audio-2025-04-24-at-10.19.26-AM.ogg?_=1
Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!