Connect with us

Labarai

Dakarun Operation Fansar Yamma sun ceto mutane 50 da shanu 32 daga hannun yan Bindiga

Published

on

Rundunar Sojin kasar nan ta Operation Fansar Yamma ta ceto wasu mutane 50 da ’yan bindiga suka yi garkuwa da su  tare da ƙwato shanu 32 da aka sace a ƙauyen Raudama, da ke ƙaramar hukumar Faskari ta jihar Katsina.

A cewar sanarwar, an sace mutanen ne ranar Lahadin da ta gabata lokacin da ’yan bindigar suka kai farmaki ƙauyen inda suka sace mutanen da kuma shanun.

Kwararren masanin nan a fannin tsaro a yankin Tafkin Chadi Zagazola Makama, ya bayyana cewa, wasu majiyoyi sun shaida masa cewa harin ya faru ne da misalin ƙarfe 8:00 na dare.

Haka kuma,ya ce, bayan harin, sojoji da ’yan sanda sun  haɗa runduna ta musamman da ta bi sawun ’yan bindigar, inda suka fafata da su.

Daga bisani ne dakarun suka samu nasarar fatattakar ’yan bindigar, tare da  ceto mutanen da aka sace,  hade da ƙwato shanun.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!